Hausa
Sorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) - Verses Number 11
وَالضُّحَىٰ 
( 1 )  
Inã rantsuwa da hantsi.
وَاللَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ 
( 2 )  
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ 
( 3 )  
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
وَلَلْآخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ الْأُولَىٰ 
( 4 )  
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰ 
( 5 )  
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَآوَىٰ 
( 6 )  
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
وَوَجَدَكَ ضَالًّا فَهَدَىٰ 
( 7 )  
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
وَوَجَدَكَ عَائِلًا فَأَغْنَىٰ 
( 8 )  
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ 
( 9 )  
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
وَأَمَّا السَّائِلَ فَلَا تَنْهَرْ 
( 10 )  
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ 
( 11 )  
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).